Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Har ila yau Hizbullahi ta ce ta kai hari kan manya bindigogi Isra'ila a kusa da wurin sojin Al-Sadh da rokoki da dama. Sannan anjiyo ƙararrawa a cikin yankunan da aka mamaye. Hizbullah ta sanar da cewa nan ba da jimawa ba za ta buga muhimman labarai game da kai hari kan wuraren sojojin Isra'ila.
Hizbullah ta sake kai hari kan matattarar sojojin sahyoniyawa da kayan aikinsu a yayin wani samame a birnin Bint Jbei tare da manyan bindigu da rokoki da dama.
Your Comment